Wata sanarwar da kamfanin dillancin labarai na Xinhua ya samu kwafin ta, ta rawaito rundunar sojojin kasar na cewa, maharan sun farwa jami'an tsaron ne a daren ranar Litinin.
Wannan hari dai ya biyo bayan wani harin da mayakan kungiyar suka kaiwa sansanin sojojin kasar dake Kukareta na birnin Damaturun jihar Yobe, jihar dake arewa maso gabashin kasar, wanda shi ma ya auku a ranar ta Litinin.