in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta zama ta biyu wajen yawan ba da kudi ga MDD
2018-12-24 14:17:50 cri
Wajen wani taron MDD da ya gudana a daren ranar 22 ga watan da muke ciki, an zartas da wani kuduri game da yadda za a raba nauyi a tsakanin mambobin MDD, na baiwa majalisar kudin gudanar da aikinta a fannonin daban daban, da na ayyukan yau da kullum gami da aikin wanzar da zaman lafiya, tsakanin shekarar 2019 zuwa ta 2021.

A fannin kudin tafiyar da ayyukan yau da kullum na MDD, kudin da kasar Sin za ta bayar, a karon farko ya zarta na kasar Japan, inda kasar ta Sin ta zama kasa ta biyu a fannin yawan baiwa MDD kudi.

An ce, kudin da kasar Sin za ta samarwa MDD don tallafawa ayyukanta na yau da kullum ya karu daga kashi 7.92%, zuwa kimanin kashi 12%, na daukacin kudin da majalisar ke bukata a wannan fanni. Sa'an nan a fannin aikin wanzar da zaman lafiya, kudin da kasar Sin ta bayar ya karu daga kashi 10.24% zuwa kashi 15.22%, wanda shi ma ya kasance na biyu cikin kudin da kasashe dabam daban ke baiwa majalisar. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China