in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tsunami ya hallaka mutane a kalla 281 a kasar Indonesia
2018-12-24 10:42:45 cri
Bala'in ambaliyar ruwan teku ta Tsunami da ya abku a kasar Indonesia sakamakon amon wuta da wani dutse ya yi ya haddasa hasarar rayukan mutane a kalla 281, yayin da wasu 843 suka jikkata, kamar yadda hukumar tinkarar bala'i daga indallahi ta kasar ta sanar a yau Litinin. Haka kuma an ce adadin zai iya karuwa bisa ci gaban aikin binciken hasarar da aka samu.

An ce tsunami ya abuku ne a daren ranar Asabar bisa agogon birnin Jakarta, bayan wani dutse mai suna Anak Krakatau ya yi amon wuta, lamarin da ya haddasa zabtarewar kasa a karkashin ruwan teku, da karuwar ruwan teku, in ji hulumar tinkarar bala'i ta kasar Indonesia.

Tsunamin ya rushe gidaje 556, da hotel 9, gami da jiragen ruwa 360, a yankin Pandeglang, inda aka samu hasara mafi tsanani, gami da sauran wasu yankuna 2, in ji Sutopo Nugroho, kakakin hukuma mai kula da aikin tinkarar bala'i ta kasar Indonesia. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China