Kakakin hukumar, Sutopo Purwo Nugrohoya ya kara da cewa, bala'in ya kuma halaka gidajen al'umma da otel da kuma jiragen ruwa masu yawa.
A jiya da dare, babbar igiyar ruwa ta tsunami ta afkawa mashigin teku na Sund dake yammacin kasar Indonesia, sai dai ba a gano aukuwar girgizar kasa ba a lokacin. Ana shakku ko zabtarewar tsaunuka a karkashin teku a sanadin dutsen Krakatau da ya yi aman wuta da kuma cikar ruwan teku a sanadin cikar wata ne suka haddasa tsunami din. (Lubabatu)