in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin: Babu wata kasar Afirka da take fama da matsalar bashi sakamakon hadin kai da kasar Sin
2018-12-19 19:51:36 cri

Madam Hua Chunying, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, ya furta a yau Laraba cewa, kasar Sin tana tsayawa kan manufarta ta nuna gaskiya, da sahihanci, da kulla hulda mai kyau, gami da samar da takamaiman sakamako, da kuma ra'ayin kasar na nuna adalci a kan moriyar juna, yayin da take hadin gwiwa da kasashen Afirka, manufofin da suka samu karbuwa tsakanin al'ummomin nahiyar Afirka, gami da amincewar gamayyar kasa da kasa.

Kafin haka, Jean Juncker, shugaban majalisar kungiyar tarayyar Turai, ya bayyana a kwanakin baya cewa, tallafin da kasar Sin ta baiwa Afirka ya sanya kasashen dake nahiyar Afirka da yawa shiga matsalar bashi fiye da kima. Dangane da wadannan kalamai, Madam Hua ta ce, babu wata kasa dake nahiyar Afirka wadda ke fama da matsalar bashi sakamakon hadin gwiwa da kasar Sin. A cewar jami'ar kasar Sin, tsarin tattalin arziki maras adalci da ake amfani da shi yanzu a duniyarmu,na daga cikin manyan dalilan da suka sababa matsalar bashi fiye da kima da wasu kasashen nahiyar ke fama da ita. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China