in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta kara hada kai da Afirka a fannoni 4 da nufin ciyar da sha'anin kawar da talauci gaba
2018-08-14 19:30:54 cri
Daraktan ofishin kawar da talauci na majalisar gudanarwar kasar Sin, mista Liu Yongfu ya bayyana cewa, kasar Sin da kasashen Afirka sun samu jerin fasahohi wajen kawar da talauci, kana bangarorin biyu za su karfafa hadin kai a fannoni guda hudu, don inganta sha'anin tare.

Liu ya bayyana haka ne a yayin taron harkokin kawar da talauci da samun ci gaba na dandalin tattaunawar hadin kai tsakanin Sin da Afirka na shekarar 2018, wanda aka shirya yau a nan birnin Beijing. Ya kara da cewa, kawar da talauci da tabbatar da samun dauwamammen ci gaba sun kasance buri da aikin bai daya na jama'ar Sin da na kasashen Afirka. Kokarin yin cudanya da hada kai a fannin kawar da talauci ita ce hanya mai muhimmanci ta tabbatar da samun ci gaba tare, da gina al'umma mai kyakyyawar makoma ga bangarorin biyu. Don haka, ya kamata su karfafa hadin kai a wadannan fannoni guda hudu, kamar kara yin musanyar ra'ayoyi, da nazari tare, da horar da kwararrun matasa, da kuma gudanar da shirye-shiryen da za su zama misali a fannin kawar da talauci. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China