Xi Jinping: Za a nace ga manufar "kasa daya, tsarin mulki 2"
Shugaban kasar Sin, Xi Jinping, ya gana da kantoman yankin musamman na Hongkong na kasar Sin Madam Carrie Lam Cheng Yuet-ngor da kantoman yankin musamman na Macao na kasar Sin Fernando Chui Sai On, wadanda suke birnin Beijing domin gabatar da bayani kan ayyukansu, da yanayin da yankunan suke ciki. A yayin ganawar, shugaba Xi ya ce, gwamnatin tsakiyar kasar Sin za ta tsaya kan manufarta ta "kasa daya, tsarin mulki 2", kana za ta goyi bayan yankunan Hongkong da Macau domin su samu sabon ci gaban kansu, da ma yadda za su ba da sabuwar gudunmawa ga ci gaban kasar Sin baki daya. (Bello Wang)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku