in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya aika da sakon taya murnar bude taron tunawa da ranar gabatar da Sanarwar Kare Hakkin Bil Adama
2018-12-10 15:12:07 cri
A yau Litinin ne, aka kaddamar da taron karawa juna sani game da sanarwar Kare Hakkin Bil Adama ta Duniya da aka gabatar shekaru 70 da suka wuce, a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin. Saboda muhimmancin wannan biki, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya aika da sakon taya murna, inda ya jaddada ma'anar Sanarwar ta tarihi, gami da tasirinta ga harkokin kare hakkin bil Adama a wurare daban daban.

A cewar shugaban, jama'ar kasar Sin na son yin hadin gwiwa da jama'ar sauran kasashe, a kokarin tabbatar da zaman lafiya, da samun ci gaba, da daidaito, da adalci, da tsarin dimokuradiyya, gami da 'yancin dan Adam. Ban da wannan kuma za a kare mutunci, da hakkin kowane bil-Adam a fannoni daban daban, da kokarin bullo da tsarin kare hakkin dan Adam mai adalci, da hakuri da ra'ayoyi daban daban, ta yadda za a raya al'ummar bil Adama mai makomar bai daya, da tabbatar da samar da yanayi mai kyau a duniyarmu. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China