in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Zimbabwe: ZANU-PF ba ta da niyar kafa gwamnatin hadin kan kasa da bangaren adawa
2018-12-13 10:04:00 cri
Shugaba Emmerson Mnangagwa na kasar Zimbabwe, ya bayyana cewa, jam'iyyar ZANU-PF mai mulkin kasar ba ta da niyyar gayyatar 'yan adawa wajen kafa gwamnatin hada kai (GNU), biyo bayan nasarar da jam'iyyar ta samu a zabukan kasar na ranar 30 ga watan Yuli.

Mnangagwa dai ya doke abokin hamayyarsa na jam'iyyar kawance ta MDC Nelson Chamisa da karamin rinjaye, inda jam'iyyar ZANU-PF ta lashe kaso 2 bisa 3 na kujerun majalisar dokokin kasar, ta kuma lashe galibin kujerun majalisun kananan hukumomin kasar, yayin da jam'iyyar MDC ta yi galaba a yankunan biranen kasar.

Sai dai kuma Chamisa da jam'iyyarsa ta MDC sun yi fatali da nasarar da Mnangagwan ya samu, inda a karshen watan Nuwamba suka shirya bore a Harare, babban birnin kasar don nuna rashin amince da sakamakon zaben da ma yanayin tabarbarewar tattalin arzikin kasar.

'Yan adawar dai na bukatar Mnangagwa da su hau teburin tattaunawa, yana mai cewa jam'iyya mai mulki ita kadai ba za ta iya magance matsalar tattalin arzikin kasar ita kadai ba. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China