in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An tabbatar da mutuwar mutane 143 sanadiyyar zazzabin Lassa a Nijeriya
2018-11-23 09:58:40 cri
Nijeriya ta tabbatar da mutuwar mutane a kalla 143 a bana, sanadiyyar barkewar zazzabin lassa, wadda ake samu a galibin kasashen yammacin Afrika.

Bayanai tsakanin watannin Junairu da Nuwamba da cibiyar takaita yaduwar cutuka ta kasar ta tattara, sun bayyana cewa mutane 3,016 ake zargin sun kamu da cutar tsakanin wancan lokaci.

Tun bayan gano bullarta a ranar 1 ga watan Janairu, an samu barkewar cutar mai haifar da matsanancin zazzabi da zubar jini, a jihohi 22 da kananan hukumomi 90 na kasar.

Kakakin cibiyar Chimezie Anueyiagu, ya shaidawa manema labarai a birnin Abuja cewa, adadin wadanda cutar ta kashe kawo yanzu ya kai kaso 22.6 bisa 100.

Ya kara da cewa, yanzu haka akwai shirye-shirye dake gudana na bitar matakan da ake amfani, tare da samar da wani muhimmin tsari da zai shafe tsawo shekaru 5 domin dakile cutar a Nijeriya.

Kakakin ya ce cibiyar da hadin gwiwar hukumar lafiya ta duniya WHO, na bincike domin gano ko akwai wata dabbar dake yada kwayar cutar.

Kasashen yammacin Afrika da suka hada da Ghana da Benin da Liberia da Saliyo ne suka ba da rahoton bullar zazzabin na lassa a bana. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China