in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na goyon bayan hadin gwiwar MDD da sassan shiyyoyi wajen kandagarki da warware rikici inji jakadan kasar
2018-12-07 10:40:50 cri
Wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Ma Zhaoxu, ya ce kasar sa za ta ci gaba da goyon bayan hadin gwiwa tsakanin MDD da kungiyar tarayyar Afirka ta AU, da ma sauran kungiyoyin sassa, da na shiyyoyi a fannin kandagarki, da kuma warware tashe tashen hankula.

Ma Zhaoxu, ya bayyana hakan ne, yayin bude mahawarar kwamitin tsaron MDD game da hadin gwiwar majalissar da sauran sassan yankunan duniya, yana mai fatan irin wannan hadin gwiwa, zai haifar da kyakkyawar dama, ta shawo kan kalubalen dake addabar yankunan bisa yanayin su.

Ya ce hukumomin yankuna, da na sassa daban daban, na da masaniyar tarihin su, da al'adun su, da ainihin halin da suke ciki. Suna kuma da dama ta zakulo dabaru mafiya dacewa na magance matsalolin su, sabanin duk wata hanya da ta sabawa hakan. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China