in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping da shugaban kasar Panama sun gana da wakilan 'yan kasuwa na kasashen su
2018-12-04 10:29:39 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaran aikinsa na kasar Panama Juan Carlos Varela, sun gana da wakilan 'yan kasuwa na kasashen biyu, wadanda ke halartar taron dandalin tattaunawa kan hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da Panama a ranar 3 ga wata a birnin Panama.

A yayin ganawar, shugaba Xi Jinping ya yi nuni da cewa, 'yan kasuwa na kasashen biyu, sun taka muhimmiyar rawa wajen raya hadin gwiwar dake tsakanin kasashen biyu, don haka ya kamata kasashen biyu sun rike damarsu, da yin kokarin fadada hadin gwiwarsu. Ya ce Sin ta bude kofa ga kasa da kasa cikin sahihanci, da yin maraba da 'yan kasuwa daga kasa da kasa, ciki har da kasar Panama a fannin zuba jari da kafa kamfanoni a kasar Sin, da kuma sa kaimi ga kamfanonin Sin, wajen fadada ayyukansu a kasar Panama, don samun bunkasuwa da wadata tare.

A nasa bangare, shugaba Varela ya yi maraba da kamfanonin Sin da su shiga kasuwannin kasarsa domin zuba jari, da maida kasar Panama a matsayin muhimmin wurin fadada ayyukansu a nahiyar Latin Amurka, da taimakawa kasar wajen samun ci gaba, da cimma burin samun moriyar juna ta hanyar hadin gwiwar da shugaba Xi Jinping ya gabatar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China