in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban sakataren MDD ya yi kira ga Rasha da Ukraine da su yi hakuri da magance tsananta halin da ake ciki a tsakaninsu
2018-11-28 10:36:43 cri
Babban sakataren MDD Antonio Guterres ya bayana a jiya cikin wata sanarwa ta hannun kakakinsa cewa, yana lura sosai da rikicin da ya kunnu kai ranar 25 ga wata a kan teku dake tsakanin Rasha da Ukraine, inda ya yi kira ga kasashen biyu da su yi hakuri tare da magance tsananta rikicin.

Rahotanni da hukumar kiyaye tsaro ta kasar Rasha da hukumar kula da kan iyaka ta kasar Crimea suka fitar sun nuna cewa, a ranar 25 ga wata, jiragen ruwan sojojin ruwa na kasar Ukraine guda biyar sun yi yunkurin ratsa zirin Kerch ba tare da samun iznin kasar Rasha ba, kasar Rasha ta dauki wasu matakai don hana jiragen ruwan kasar Ukraine shiga yankin ruwan.

Wani rahoto da ma'aikatar watsa labarun kasar Ukraine ta bayar, na cewa, jiragen ruwan yaki biyu da wani jirgin ruwan sojojin ruwan kasar Ukraine sun yi yunkurin ratsa zirin Kerch a kokarin shiga tekun Bahar Asuwad ta tekun Azov a ranar 25 ga wata. Wani jirgin ruwan yaki na kasar Rasha ya ci karo da jirgin ruwan sojojin ruwan Ukraine, tare da kai hari ga wani jirgin yaki na kasar Ukraine, lamarin da ya haddasa raunatar mutane 6. Daga bisani Rasha ta kama jiragen ruwan kasar Ukraine guda uku.

Bayan faruwar lamarin, Rasha da Ukraine sun dauki wasu matakai, hakan ya sa aka samu tsanantar halin da ake ciki a tsakaninsu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China