in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya yi kira da a kara gudanar da ayyukan kiyaye zaman lafiya na MDD a Afirka
2018-11-21 20:11:26 cri
Zaunannen wakilin Sin dake MDD Ma Zhaoxu ya yi jawabi a gun muhawarar da kwamitin sulhun MDD ya gudanar game da batun kara gudanar da ayyukan kiyaye zaman lafiya a Afirka, inda ya yi kira da a kara yin kokarin gudanar da ayyukan kiyaye zaman lafiya na MDD a Afirka, da zurfafa dangantakar abokantaka da kungiyar AU wajen kiyaye zaman lafiya tare.

Ma Zhaoxu ya bayyana cewa, gwamnatin kasar Sin da jama'arta suna goyon bayan kasashen Afirka da jama'arsu da su yi kokarin neman samun zaman lafiya da wadata da ci gaba. Kasar Sin ta shiga ayyukan kiyaye zaman lafiya na MDD a nahiyar Afirka. Kana kasar Sin za ta ci gaba da nuna goyon baya ga kasashen Afirka kan yadda za su inganta karfinsu na kiyaye zaman lafiya da taimaka musu wajen warware matsalolin da yankin ke fuskanta cikin hanzari. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China