in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hadin gwiwar Sin da Gambia na da ban sha'awa in ji jakadan Sin
2018-11-23 11:15:59 cri
Sabon jakadan kasar Sin a kasar Gambia Ma Jianchun, ya ce hadin gwiwar dake tsakanin kasar sa da Gambia na da matukar burgewa. Ma ya bayyana hakan ne, yayin liyafar maraba da zuwa, wadda gwamnatin Gambia ta shirya masa a jiya Alhamis.

Ya ce Sin da Gambia, na hadin gwiwa a sassa masu tarin yawa, kuma abun farin ciki ne, ganin yadda ake ci gaba da raya hadin kai, da samar da karin ayyuka tsakanin kasashen. Jami'in ya ce hanyoyin mota, da gadoji, wadanda kasar Sin ta tallafa wajen ginawa a kasar, kuma ake fatan kaddamarwa cikin wata mai zuwa, misali ne na irin gajiyar da hadin gwiwar ya haifar.

Kaza lika a cewar sa, tsare tsaren nan guda 8 na hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka karkashin dandalin FOCAC, sun dace da manufofin raya kasa na gwamnatin Gambia.

Daga nan sai Mr. Ma ya bayyana shigar kasar Gambia dandalin FOCAC, a matsayin matakin shiga babban iyalin wannan dandali, kuma a cewar sa ko shakka babu, Gambia za ta ci gajiya maras iyaka daga sakamakon taron dandalin da ya gudana a birnin Beijing. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China