in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta bayyana bukatar kara tallafawa masu wanzar da zaman lafiya a Afirka
2018-11-21 10:45:58 cri
Babban magatakardar MDD Antonio Guterres, ya bukaci a tallafawa rundunonin dake aikin wanzar da zaman lafiya a yankunan nahiyar Afirka, kasancewar kalubalen tsaro dake addabar nahiyar ya shafi tsaron duniya ne baki daya.

Mr. Guterres ya yi kiran ne a jiya Talata, yayin zaman kwamitin tsaron MDD. Ya ce dalilan da suke haddada tashe tashen hankula a nahiyar Afirka sun hada da talauci, da rashin ayyukan yi tsakanin matasa, da tasirin sauyin yanayi, da takara wajen cin gajiyar albarkatu, da laifuka na kasa da kasa, wadanda dukkanin su ke barazana ga tsaron kasa da kasa.

A don haka ne jami'in ya bayyana cewa, kyautata ayyukan wanzar da zaman lafiya a Afirka, nauyi ne da ya rataya a wuyan daukacin sassan duniya.

Babban magatakardar MDDr ya kara da cewa, ya kamata duniya ta san irin tarin nauyi da ke wuyan jami'an MDD masu aikin wanzar da zaman lafiya. Kaza lika a cewar sa, MDD na fuskantar kalubale da dama, a fannin ayyukan yaki da 'yan ta'adda, wanda dole ne sai ta yi hadin gwiwa da abokan huldar ta irin su kungiyar AU da makamantan ta, kafin ta kai ga cimma nasarar shawo kan matsalolin.

Don haka dai Mr. Guterres na ganin cewa, akwai bukatar ba da gudummawa ga kungiyoyin nahiyar Afirka daban daban, ciki hadda kungiyar kasashen yankin Sahel su 5, dake yaki da ta'addanci. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China