in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta bukaci nahiyar Afrika ta dauki matsaya guda yayin da huldar kasa da kasa ke tabarbarewa
2018-11-19 10:36:01 cri
Shugaban hukumar AU Moussa Faki Mahamat, ya yi kira ga kasashe mambobin kungiyar, su samar da matsaya guda ta nahiyar, la'akari da yadda duniya ke fuskantar koma baya a bangaren huldar kasa da kasa.

Moussa Faki Mahamat, ya bayyana haka ne yayin rufe taron kungiyar da ya gudana daga ranar 17 zuwa 18 ga wata, a hedkwatar kungiyar dake Addis Ababa na Habasha .

Ya kara da cewa, harkokin duniya na sauyawa, don haka ya kamata a samar da matsaya guda ta nahiyar tare da yin magana da murya guda.

Ya kuma bayyana cewa tabarbarewar alakar kasa da kasa da ke zama abun damuwa a duniya, ya haifar da bukatar samar da matsaya guda ta nahiyar.

A cewarsa, yayin da sauye- sauyen al'amuran duniya a yanzu ke tasiri kan nahiyar, bukatar tabbatar da 'yancin kan kungiyar AU da ma nahiyar baki baya, abu ne mai muhimmanci.

Har ila yau, Faki Mahamat, ya bayyana yayin taron majalisar zartarwar kungiyar na 20 da aka yi ranar Larabar da ta gabata cewa, sauyen sauyen da ake fuskanta na nuni da bukatar karfafa kungiyar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China