in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU na fatan inganta tsaro da zaman lafiya a Afrika karkashin wani sabon shiri
2018-11-19 10:13:48 cri
An kaddamar da asusun wanzar da zaman lafiya na Tarayyar Afrika AU, a wani bangare na taron tarayyar, inda shugabannin nahiyar karkashin inuwar tarayyar, ke da burin inganta zaman lafiya da tsaro a fadin nahiyar.

Asusun da aka kaddamar a baya-bayan nan tare da wasu shirye-shirye, sun ta'allaka ne kan manyan batutuwa 3, da suka hada da rungumar shirye shiryen sulhu da matakan kare barkewar rikici da inganta ayyukan kungiyar da kuma taimakawa ayyukan wanzar da zaman lafiya.

Asusun na wanzar da zaman lafiya a nahiyar, wanda tuni aka kafa masa kwamitin amintattu mai mabobi 5 da kuma jagoransu, zai fara aiki ne da kudi dala miliyan 100.

Shugaban Rwanda kuma shugaban Tarayyar mai ci wato Paul Kagame, ya bayyana yayin bikin kaddamar da asusun a ranar Asabar cewa, asusun zai yi aiki ne wajen tabbatar da zaman lafiya da shawo kan kalubalen tsaro bisa matakan nahiyar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China