Xi Jinping ya tashi daga Beijing don halartar taron shugabanni na APEC
A yau Alhamis ne, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya tashi daga birnin Beijing, don kai ziyara kasashen Papua New Guinea, Brunei, Philippines bisa gayyatar gwamnan Papua New Guinea kuma firaministan kasar Peter O'Neill, da sarki Hassanal Bolkiah na kasar Brunei, da shugaban kasar Philippines Rodrigo Duterte suka yi masa, kana zai gana da shugabannin kasashen tsibiran tekun Pasifik da suka kulla dangantakar diplomasiyya tare da kasar Sin. Kana bisa gayyatar da firaministan kasar Peter O'Neill ya yi masa, shugaba Xi Jinping zai halarci taron shugabannin kungiyar APEC karo na 26 da zai gudana a mashigin tekun Moresby dake kasar Papua New Guinea. (Zainab)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku