in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Xi ya jagoranci zama na 5 na kwamitin kolin JKS game da zurfafa gayare gyare daga dukkanin fannoni
2018-11-14 21:14:33 cri
A Larabar nan ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya jagoranci zama na 5, na kwamitin koli, game da zurfafa gyare gyare daga dukkanin fannoni.

Shugaba Xi wanda kuma shi ne babban sakataren kwamitin kolin JKS, kana shugaban hukumar zartawar rundunar sojojin kasar, kuma shugaban kwamitin koli game da zurfafa gyare gyare daga dukkanin fannoni na kasar, ya yi kira da a kara azama, wajen yin gyare-gyare a gida da bude kofa ga kasashen waje, da kokarin cimma manyan nasarori a fannin ingantawa, da bunkasa tsarin mulkin gurguzu mai halayyar musamman na Sin, da zamanantar da salon aiwatar da manufofin gwamnatin kasar.

Kaza lika ya bukaci sassan masu ruwa da tsaki, da su kara zage damtse wajen aiwatar da gyare-gyare, da kara bude kofa a sabon zamani da ake ciki.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China