in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Xi ya yi kira da a karfafa gwiwa domin fadada gyare-gyare da bude kofa
2018-11-13 20:21:12 cri

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya bukaci da a dauki karin matakan karfafa gwiwa da juriya, wajen aiwatar da manufofin yin gyare-gyare a cikin kasar Sin da kuma bude kofar kasar ga kasashen waje. Shugaba Xi ya yi wannan kira ne a Talatar nan.

Shugaba Xi, wanda kuma shi ne babban sakataren kwamitin koli na JKS, kuma shugaban hukumar zartaswar rundunar sojojin kasar, ya halarci wani muhimmin baje kolin nune nune, wanda aka shirya domin murnar cika shekaru 40 da fara aiwatar da manufar gyare gyare a gida, da bude kofa ga kasashen waje.

Ya kuma bayyana cewa, baje kolin zai taimaka wajen cimma daidaito, da karfafa gwiwar juna, tare da bunkasa hadin kai, da zaburar da karin ci gaban kasa.

A Talatar ne aka bude baje kolin nune nune, game da manufofin kasar Sin na aiwatar da gyare-gyare a gida, da bude kofa ga kasashen waje a nan birnin Beijing, domin murnar cika shekaru 40 da aiwatar da manufofin.

Yayin baje kolin an gabatar da hotuna, da rubatattun bayanai, da faya fayen bidiyo, da ayyukan cudanya da baki mahalarta da sauransu, domin nuna irin matakai da kasar Sin ta bi wajen kaiwa ga gagarumin ci gaban ta na yanzu, da wanda take fatan samu nan gaba.

Kimanin mutane 1,000 ne dai suka halarci bikin bude baje kolin.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China