in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Xi ya yi fatan yankunan Hong Kong da Macao za su rungumi gyare-gyare da bude kofa domin bunkasa ci gaba
2018-11-12 21:00:42 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya bayyana fatan yankunan Hong Kong da Macao, za su rungumi manufar yin gyare-gyare a gida, da bude kofa ga kasashen waje, domin bunkasa ci gaban kasar Sin baki daya.

Shugaba Xi ya yi wannan tsokaci ne a Litinin din nan, yayin da yake zantawa da wakilan yankunan biyu. Ya ce yana da burin ganin 'yan uwa na yankunan biyu sun shiga adama da su, wajen aiwatar da wadannan manufofi masu fa'ida, da sahihiyar zuciya da kishin kasa, ta yadda hakan zai fadada ci gaban yankunan na musamman, tare da taka tasu rawa, wajen kara farfadowar kasar Sin baki daya.

Wakilan yankunan nan Hong Kong da Macau, sun ziyarci birnin Beijing, babban birnin kasar ne domin murnar cika shekaru 40, da fara aiwatar da manufar gudanar da gyare gyare a gida, da bude kofa ga kasashen waje ta kasar.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China