in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wang Yi: Bai kamata a saurara labari maras tushe game da harkokin jihar Xinjiang ba
2018-11-14 10:30:30 cri
Memban majalisar gudanarwar kasar Sin kuma ministan harkokin wajen kasar Wang Yi ya amsa tambayar da aka yi masa game da cibiyar horar da kwararru dake jihar Xinjiang ta kasar Sin da 'yan jaridan kasar Jamus suka yi masa bayan da ya yi shawarwari tare da ministan harkokin wajen kasar Jamus Heiko Maas a jiya Talata.

Wang Yi ya bayyana cewa, harkokin jihar Xinjiang harkokin cikin gida ne na kasar Sin. Yana fatan 'yan jarida su rika ba da muhimmanci ga labarin da Sin ta gabatar a hukunce, wato labarin da gwamnatin jihar Xinjiang ta gabatar, bai kamata a rika sauraron labarai maras tushe daga wasu bangarori game da wannan batu ba.

Wang Yi yana fatan 'yan jarida za su fahimta da nuna goyon baya ga kokarin da gwamnatin jihar Xinjiang ta yi wajen yaki da ta'addanci da masu tsattsauran ra'ayi da tabbatar da zaman lafiya a jihar da tsaron jama'ar yankin gaba daya. Kokarin ya yi daidai da manufar yaki da ta'addanci ta kasa da kasa, kuma shi wani muhimmin bangare ne na aikin yaki da ta'addanci a duniya. Musamman jihar ta hada aikin yaki da ta'addanci da aikin magance ta'addanci, kana ana daukar aikin magance ta'addanci da muhimmancin gaske. Idan aka gudanar da aikin magance ta'addanci yadda ya kamata, za a kawar da bullar masu ra'ayin ta'addanci daga tushe, wannan ita ce hanya mafi dacewa wajen yaki da ta'addanci. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China