in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Habasha zata karbi bakuncin kamfanoni 230 na cikin gida da na waje a bikin baje kolin kasar
2018-11-01 10:41:05 cri
Sama da kamfanoni 230 na cikin gida da na kasa da kasa ne suka kammala shirye shiryen halartar bikin baje kolin kasa da kasa na Habasha, jami'in shirya bikin ne ya tabbatar da hakan.

Bikin baje kolin na kasa da kasa na Habasha za'a gudanar da shi ne daga ranar 1 zuwa 5 ga wannan wata na Nuwamba, zai samu halartar kamfanonin cikin gida da na kasashen waje da suka hada da kasashen Sin, Girka, Rasha, India, Singapore, Masar, Saudi Arabia, Hadaddiyar daular larabawa, da kuma Iran, jami'in shirin daga majalisar ciniki da zuba jari ta kasar Habashan (ECCSA), shine ya tabbatar da hakan a jiya Laraba.

Kafanonin da zasu halarci bikin daga kasashen Afrika sun hada da Sudan, Somalia da Morocco da dai sauransu, zasu bi sahun mahalarta bikin na tsawon kwanki 5, wanda za'a baje kolin kayayyaki da masu aikin bada hidima zasu taru a Addis Ababa, babban birnin kasar, in ji jami'in na ECCSA.

Masu zuba jari daga kasashen waje zasu yi amfani da wannan dama wajen shiga kasuwannin kasar Habashan, inji sakatare janar na majalisar ECCSA, Endalkachew Sime.

Ya kara da cewa, bikin baje kolin wata babbar dama ce ga kasar ta gabashin Afrika wajen jawo hankalin masu zuba jari daga kasashen waje zuwa kasar. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China