in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin Sin da Faransa sun taya wa juna murna kan yadda aka harba wani tauraron dan Adam cikin nasara
2018-10-29 14:01:28 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na kasar Faransa Emmanuel Macron, sun yi musayar sakwanni a yau Litinin, don taya juna murnar cimma nasarar harba tauraron dan Adam na binciken yanayin teku, wanda kasashen su, suka yi hadin gwiwar samar da shi.

Cikin sakonsa, shugaba Xi na kasar Sin ya ce hadin gwiwar da ake yi a fannin zirga-zirgar kumbuna, wani muhimmin bangare ne na abotar dake tsakanin Sin da Faransa, wadda ta shafi dukkan fannoni.

A nasa bangare, shugaba Macron na kasar Faransa, ya ce nasarar da aka samu a wannan karo, ta shaida ci gaban da aka samu a hadin gwiwar da ake yi tsakanin Faransa da Sin, musamman ma a fannin zirga-zirgar kumbuna. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China