in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya sake yin rangadin aiki a lardin Guangdong
2018-10-23 13:15:55 cri
A jiya ranar 22 ga wata da yamma, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya isa birnin Zhuhai dake lardin Guangdong na kasar Sin, wanda ya sake yin rangadin aiki a lardin Guangdong bayan shekaru 6.

Xi Jinping ya kai ziyara yankin fasahohin zamani na Hengqin dake birnin Zhuhai da farko, wannan ne karo na 4 da Xi Jinping ya kai ziyara a wurin a cikin shekaru 10 da suka gabata.

Xi Jinping ya bayyana cewa, a cikin shekaru 10 da suka gabata, ana samun babban canji a yankin Hengqin. Ya kamata mu tuna da burinmu na farko, da kara yin kirkire-kirkire, da sa kaimi ga samun bunkasuwar tattalin arziki a fannoni daban daban a yankin Macau.

Bayan da ya tashi daga yankin Hengqin, sai shugaba Xi Jinping ya kai ziyara a kamfanin GREE, wanda ya samar da na'urorin sanyaya daki, da na'urorin zamani, da kuma na'urorin amfanin yau da kullum, kana an sayar da su a kasashe da yankuna fiye da 160 a duniya.

Xi Jinping ya jaddada cewa, ya kamata kamfanonin Sin su ci gaba da kokarin yin kirekire-kirkire da kansu, da inganta karfinsu a wannan fanni. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China