in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamfanin Sin ya zuba jari don gina kamfanin kera fadi-ka-mutu a kasar Zimbabwe
2018-10-23 10:30:43 cri

A jiya ranar 22 ga wata, an yi bikin aza tubalin gina kamfanin kera fadi-ka-mutu da kamfanin Sin ya zuba jari a kasar Zimbabwe. Ana shirin zuba jari dala miliyan 120 wajen gina kamfanin kera fadi-ka-mutu na Yangguangyifeng na kasar Zimbabwe, wanda zai samar da kayan fadi-ka-mutu da sauransu.

Mukaddashin jakadan Sin dake kasar Zimbabwe Zhao Baogang ya halarci bikin tare da yin jawabi, inda ya bayyana cewa, kasar Sin aminiya ce ta kasar Zimbabwe, wadda ta samar da taimako da dama wajen raya kasar Zimbabwe. Yanzu kasar Zimbabwe tana kokarin kawar da yanayin raguwar bunkasuwar tattalin arziknta, gina kamfanin zai taimakawa kasar Zimbabwe wajen raya tattalin arziki da amfanawa jama'a tare da sa kaimi ga raya dangantakar dake tsakanin Sin da Zimbabwe.

An ce, kamfanin zai samar da ayyuka fiye da dubu daya ga kasar Zimbabwe. Yanzu ana gina kamfanin, ana sa ran za a gama gina shi da fara kera fadi-ka-mutu a tsakiyar shekarar badi. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China