in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Zimbabwe ta ayyana matakin ta baci a babban birnin kasar sanadiyyar barkewar cutar Kwalara
2018-09-12 10:17:48 cri
Gwamnatin Zimbabwe ta ayyana matakin ta baci kan barkewar cutar kwalara a Harare babban birnin kasar.

Kawo yanzu, cutar da ta barke a makon da ya gabata a ungunwannin dake Glen View da Budiriro dake yawan al'umma, ya yi sanadin mutuwar mutane 20, yayin da 2,000 suka kamu da ita, kana ta kuma barke a wasu sassa na kasar.

Sabon Ministan lafiya na kasar Obadiah Moyo, ya shaidawa manema labarai cewa, gwamnati ta dauki matakan dakile yaduwar cutar, ciki har da hana tallar kifi da nama da kuma dakatar da karatu a wasu makarantun dake yankunan da cutar ta barke.

Ya ce an samu barkewar cutar ne sanadiyyar fashewar bututan kawar da najasa, abun da ya bata ruwan rijiyoyin burtsatsai da sauran rijiyoyin da mazaunan wurin ke amfani da su.

Yawancin mutanen da ke yankunan dake da yawan jama'a sun dogara ne kan ruwan rijiyoyi da na burtsatsai, saboda rashin samun tsafatatacen ruwa akai akai.

Ministan ya ce Gwamnati ta nemi taimakon hukumomin MDD da na kamfanoni masu zaman kansu, domin su samar da ruwa ga al'ummar yankunan da cutar ta barke.

Kafin wannan, lokaci na karshe da Zimbabwe ta fuskanci barkewar cutar kwalara shi ne shekarar 2008, inda ta yi sanadin mutuwar mutane 4,000 yayin da kusan 100,000 suka kamu da ita. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China