in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin tsaro na MDD ya yabawa yarjejeniyar da MDD da Mali suka cimma game da aiwatar da yarjejeniyar zaman lafiya a kasar
2018-10-20 15:58:48 cri
Kwamitin tsaro na MDD, ya yabawa yarjejeniyar da aka rattabawa hannu tsakanin gwamnatin Mali da MDD, wadda ke da nufin mara baya ga aiwatar da yarjejeniyar zaman lafiya ta kasar Mali ta 2015.

Cikin wata sanarwa da ya fitar, kwamitin ya jinjinawa tanade-tanaden yarjejeniyar da aka sanyawa hannu ranar Litini da ta gabata, wadanda suka jaddada kudurin MDD na bada cikakken goyon baya ga aiwatar da yarjejeniyar zaman lafiya da sulhu a kasar Mali.

Kwamitin ya kuma yi maraba da sabon kudurin gwamnati da na kungiyoyin masu dauke da makamai, na gaggauta aiwatar da yarjejeniyar, inda ya yi kira ga dukkan masu ruwa da tsaki su hada karfi da karfe don inganta samar da zaman lafiya mai dorewa da kare hakkokin bil adma da magance kalubalen tsaro da na ci gaba. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China