in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a bayyana sakamakon zaben shugaban kasar Kamaru a ranar Litinin
2018-10-20 15:56:02 cri
Majalisar kula da kundin tsarin mulkin Kamaru, ta bayyana a jiya cewa, za ta sanar da sakamakon zaben shugaban kasar a ranar Litinin.

Sanarwar da majalisar ta fitar a jiyan, ta cewa za a fara bikin sanar da sakamakon ne a da karfe 11 na safiyar ranar Litinin, agogon kasar.

Majalisar ta gayyaci jami'an gwamnati da jakadu da hukumomin kasa da kasa domin halartar taron da za a yi a babban dakin taro na birnin Yaounde.

Da safiyar jiya Juma'a ne majalisar ta kori kara ta karshe cikin 18 da aka shigar gabanta, wadanda ke bukatar soke zaben na ranar 7 ga wata.

'Yan takarar 8 ne suka fafata da shugaban kasar mai ci Paul biya mai shekaru 85, wanda ke neman zarcewa cikin wani sabon wa'adi na shekaru 7. (Fa'iza Msutapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China