in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An mika sakamakon zaben shugaban kasar Kamaru ga majalisar kula da kundin tsarin mulkin kasar
2018-10-16 10:24:19 cri
Hukumar kidaya kuri'un zabe ta Kamaru, ta mika sakamakon zaben shugaban kasa da aka yi ranar 7 ga wata, ga majalisar kula da kundin tsarin mulkin kasar.

Bisa tanadin dokar zaben kasar, majalisar ce ke da hakkin amincewa da bayyana sakamakon zabe cikin kwanaki 15 da kammala kada kuri'u.

Sanarwar da Sakatare Janar na majalisar, Malego Joseph Asse ya fitar, ta ce a yau Talata ne majalisar za ta fara sauraron korafe-korafe daga wasu 'yan takarar jam'iyyun adawa da kuma masu kada kuri'a dake bukatar a soke zaben.

Daga cikin wadanda suka shigar da kara kotu, akwai 'yan takara masu adawa 3, wadanda ke bukatar a soke wani bangare ko kuma baki dayan zaben, suna masu dogaro da kurakurai da magudi da suka lura an tafka yayin zaben.

Haka zalika, dokar zaben ta yi tanadin cewa, majalisar kula da kundin tsarin mulkin kasar ce za ta yanke hukunci na karshe game da zaben da kuma sakamakonsa. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China