in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin kundin tsarin mulkin Kamaru ya yi watsi da daukacin kararrakin da aka gabatar masa
2018-10-19 19:28:22 cri
A yau Juma'a ne kwamitin kundin tsarin mulkin kasar Kamaru, yayi watsi da daukacin kararrakin da aka gabatar masa, na neman a soke sakamakon babban zaben kasar da ya gudana a ranar 7 ga watan Oktoban da ya gabata.

A wannan rana, kwamitin ya kori karar da 'dan takarar jam'iyyar adawa ta SDF Joshua Osih ya shigar gaban sa, yana mai bukatar a soke zaben shugaban kasar da aka kada.

Watsi da wannan kara dai ya kawo karshen zaman sauraren korafe korafe da kwamitin ya kwashe kwanaki 4 yana yi, inda ya saurari koke koke 18, wadanda kuma dukkanin su kwamitin ya ce ba su da hujja mai karfi. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China