in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Kamaru ta yi watsi da ikirarin cin zaben shugaban kasar da dan takarar jam'iyyar adawa ya yi
2018-10-09 09:44:50 cri
Ministan kula da yankuna na Kamaru, Paul Atanga Nji, ya bayyana a jiya cewa, ikirarin lashe zaben shugaban kasar da aka yi ranar Lahadi daga wani dan takara, abu ne da ya sabawa kundin tsarin mulkin kasar.

Paul Nji, ya ce majalisar kula da kundin tsarin mulkin kasar ce kadai ke da ikon bayyana sakamakon zaben, ba wani ba mutum ba.

Wannan na zuwa ne bayan Maurice Kamto, dan takarar jam'iyyar adawa, ya yi ikirarin samun nasara a zaben.

Yayin wani taron manema labarai a birnin Yaounde, Maurice Kamto, ya ce al'ummar Kamaru sun riga sun nuna abun da suke so a bayyana, kuma ya yi niyyar kare Muradin na su har zuwa karshe. A don haka, yake kira ga shugaban kasar mai barin gado, ya shirya mika mulki cikin lumana domin kaucewa duk wani rikicin bayan zabe. Yana mai cewa jam'iyyarsa za ta daukaka zaman lafiya.

Bisa dokokin zaben Kamaru, majalisar kula da kundin tsarin mulkin kasar ce za ta bayyana sakamakon zaben a hukumance, cikin kwanaki 15 bayan kammaluwarsa. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China