in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ce kan gaba wajen samun jarin kasashen ketare a rabin farko na bana
2018-10-16 11:11:20 cri
Hukumar bunkasa cinikayya da ci gaba ta MDD, ta ce kasar Sin ce ta fi kowacce a duniya samun jarin kai tsaye na ketare cikin rabin farko na bana, wanda ya kai dala biliyan 70.

Rahoton da hukumar ta wallafa wanda ya yi nazarin yanayin harkokin zuba jari, ya ce adadin jarin da ake zubawa a kasashen ketare ya sauka da kaso 41 cikin dari, zuwa dala biliyan 470, daga dala biliyan 794 da ya kasance a makamancin lokacin a shekarar 2017.

Rahoton ya alakanta koma bayan da aka samu da matakin da kamfanonin Amurka suka dauka na karbo ribarsu da ya taru daga rassansu dake kasashen ketare, biyo bayan sauyin tsarin haraji.

Daraktan sashen zuba jari da kasuwanci na hukumar James Zhan, ya ce ana samun karuwar zuba jari a kasar Sin duk da takkadamar cinikayya da karuwar farashin sarrafa kayayyaki.

Kasar Sin ce kan gaba wajen samun jarin kasashen ketare, inda adadin ya karu da kaso 6, Birtaniya ke rufa mata baya da dala biliyan 66, sai Amurka da ta samu jarin dala biliyan 46. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China