in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwararru a Afirka sun yi kira da a zage damtse game da karuwar zafi don ceto rayuwar al'umma
2018-10-12 10:09:37 cri
Masana sun yi kira ga gwamnatoci da masana'antu da su kara zage damtse wajen rage fitar da abubuwa masu gurbata yanayi, a wani mataki na rage karuwar zafin dake barazana ga rayuwar bil-Adama da ma albartakun dake nahiyar Afirka.

Masanan sun yi wannan kiran ne yayin taron kolin nahiyar kan yanayi da ya gudana a birnin Nairobin kasar Kenya. Sun kuma amince cewa, makomar al'ummomin nahiyar na cikin garari duba da yadda dumamar duniya ke haddasa fari da karancin abinci da ma bullar sabbin cututtuka da lalacewar muhallin halittu.

Wani masani dan kasar Habasha kana mutumin da ya jagoranci tawagar MDD mai kula da harkokin gwamnatoci kan sauyin yanayi(IPCC) kan wani rahoto na musamman game da dumamar yanayin duniya Yacob Mulugetta, ya bayyana cewa, karuwar zafi za ta iya mayar da ci gaban da kasashen na Afirka su ka samu a fannonin jin dadin jama'a da tattalin arziki baya.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China