in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministocin muhalli na Afirka sun kuduri aniyar kirkiro matakan magance matsalar muhalli
2018-09-20 11:15:30 cri
A jiya ne ministocin kula da muhalli daga kasashen Afirka suka kammala wani taro na kwanaki uku a birnin Nairobin kasar Kenya, inda suka yanke shawarar amfani da matakan kirkire-kirkire wajen shawo kan kalulabalen muhalli da kasashen su ke fuskanta.

Bugu da kari, ministocin sun amince su kara inganta kwarewar ma'aikata ta yadda za a samu ci gaba mai dorewa a Afirka da zuba jari a fannonin kirkire-kirkire don canja hanyar samun bunkasuwa ta yadda za a kai ga samun ci gaba mai dorewa, maimakon matakan da ake amfani da su a halin yanzu da ba sa samar da sakamako mai kyau cikin hanzari.

Ministocin sun kuma amince su goyi bayan tsare-tsare game da muhalli na kasashen Afirka don yayata da musayar kwarewa da mafita a sassa daban-daban na nahiyar. Za kuma su kara karfin kasashensu wajen aiwatar da manufofi da dokoki da shirye-shirye don karfafa matakai da sauran shirye-shiryen kula da muhalli.

Daga karshe ministocin sun yi kira ga babban taron MDD kan muhalli da shirin kare muhalli na MDD da su kara goyon bayan da suke baiwa kasashen Afirka da ma saukaka musu hanyoyin yin hadin gwiwa a fannin kirkire-kirkire.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China