in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Uwargidan shugaban kasar Sin ta aike da sakon taya murna ga bikin karrama masu fafutukar ilimin mata da 'yan mata
2018-10-12 09:59:42 cri
Uwargidan Shugaban kasar Sin Peng Liyuan, kuma wakiliyar musammam ta bunkasa ilimin mata da 'yan mata ta hukumar UNESCO, ta aike da sakon taya murna ga bikin karrama masu fafutukar ilimin mata da 'yan mata na UNESCO karo na 3, wanda ya gudana jiya a birnin Paris.

Peng Liyuan ta aike da sakon fatan alkhairi ga wadanda suka samu kyautukan a bana, wadanda suka hada da Gidauniyar Misr El Kheir ta Masar da kuma Gidauniyar Mata ta Jamaica.

A cikin sakon nata, ta ce ilimin mata da 'yan mata babban jigo ne wajen karfafa musu samun damarmakin cimma nasara a harkokinsu kamar takwarorinsu maza. Haka zalika ta ce muhimmiyar hanya ce, kana wani bangare ne na cimma muradun ci gaba masu dorewa na MDD da ake son cimmawa ya zuwa 2030.

Har ila yau, ta ce kyautar hukumar UNESCO ga masu fafutukar ilimin mata da 'yan mata, ta taka muhimmiyar rawa wajen karfafawa karin mutane gwiwar dukufa ga aikin. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China