in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Trump yana nazari kan wanda zai maye gurbin Haley a matsayin jakadan Amurka a MDD
2018-10-11 09:29:43 cri
Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya sanar a jiya Laraba cewa gwamnatinsa tana tuntubar Dina Powell, tsohuwar babbar mai ba shi shawara, a matsayin wadda za ta gaji Nikki Haley a mukamin sabuwar jakadiyar Amurka a MDD, ko da yake hakan ba zai hana a nada wasu mutanen a kan wannan mukami ba.

Trump ya fadawa 'yan jaridu a White House cewa, Powell, tsohuwar babbar mai ba shi shawara a kan harkokin tsaro, ita ce wacce ake magana a kanta, a lokacin da aka tambaye shi ko ita ce take sahun gaba cikin jerin mutanen da ake sa ran za su gaji Haley, wacce ta sanar da yin murabus dinta a ranar Talata.

A ranar Talata ne, Trump ya bayyana cewa ya riga ya tanadi sunayen mutane 5 wadanda ake sa ran daga cikinsu za'a nada wannan mukami. Ana sa ran shugaban zai bayyana sunan sabon jakadan Amurka a MDDr cikin makonni biyu ko uku masu zuwa.

Trump ya amince da yin murabus din Haley a ranar Talata, sai dai za ta cigaba da zama kan wannan mukami har zuwa karshen shekarar nan da muke ciki.

Powell ta koma Goldman Sachs da aiki a matsayin babbar jami'a bayan da ta bar aiki da fadar White House a farkon wannan shekara. Ta taba yin aiki da gwamnatin George W. Bush. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China