in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Trump zai nada sabon jakadan Amurka a MDD nan da mako biyu ko uku
2018-10-10 09:37:42 cri
Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya fada a jiya Talata cewa nan makonni biyu ko kuma makonni uku masu zuwa zai sanar da sabon jakadan Amurka a MDD bayan da madam Nikki Haley ta yi murabus.

"Za mu sanar da wanda zai gaje ta cikin makonni biyu ko uku masu zuwa, ko kuma nan ba da jimawa ba," Trump ya fadawa 'yan jaridu a lokacin da yake sanar da yin murabus din Nikki Haley a gaban idonta.

"Muna da mutane masu yawa wadanda suke son yin wannan aikin," in ji Trump.

Haley za ta ci gaba da kasancewa a kan wannan mukami har zuwa karshen shekarar nan, wanda zai cika shekaru biyu da fara aikinta a wannan matsayi. Trump ya fada cewa dama Haley ta sanar da shi tun watanni 6 da suka wuce game da aniyarta na yin murabus din.

"Ban tsara wani abu dangane da inda nake son komawa ba" in ji tsohuwar gwamnan South Carolina a lokacin da ta shedawa manema labarai.

Haley, mai shekaru 46 da haihuwa, an tabbatar da ita ne a matsayin jakadar kasar Amurka a MDD tun bayan rantsar da shugaba Trump a watan Janairun 2017. Ana kallonta a matsayin daya daga cikin na hannun daman mista Trump da suke dasawa. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China