Jaridar Elnashra mai wallafa labaranta a intanet, ta ruwaito Abbas Ibrahim na cewa, hukumar na bada tsaro da mafaka, baya ga yafiyar haraji ga 'yan gudun hijirar dake zaune a kasar ba bisa ka'ida ba, domin gaggauta komawarsu gida.
Ya ce hukumomin tsaron Lebanon na aiki da hukumar MDD mai kula da 'yan gudun hijira domin tabbatar da mutane sun koma gida lafiya, kuma bisa radin kansu.
Ya kuma yabawa yunkurin hukumomin Rasha dangane da aikin.
Domin mayar da 'yan gudun hijirar kasarsu, Rasha ta gabatar da wani kuduri ga hukumomin tsaron Lebanon, wanda ke da nufin tabbatar da komawar 'yan gudun hijira 890,000 zuwa Syria. (Fa'iza Muistapha)