in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Botswana na neman fadada fitar da naman sa zuwa kasuwar kasar Sin
2018-10-08 10:20:24 cri
Ministan raya aikin gona da wadatuwar abinci na Botswana Patrick Ralotsia, ya ce kasar na neman shigar da naman sa da dangoginsa kasuwar kasar Sin, bisa dabarunta na fadada harkokin fitar da kayayyaki.

Da yake ganawa da makiyaya a Francistown, birni mafi girma na 2 a kasar, Ministan ya ce gwamnati na duba yuwuwar fadada kasuwarta na fitar da naman sa.

Botswana kan samar da akalla ton 24,000 na naman sa a kowacce shekara ta hannu kamfaninta dake sarrafa nama, inda take sayarwa da shi a ciki da wajen kasar.

Kimanin ton 9,000 na naman ake fitarwa nahiyar Turai, kuma kasar a yanzu, na son sayar da naman a karin kasuwanni dake yankinta da ma duniya baki daya.

A don haka ne Ministan ya ce kasar ta dauki wani lokaci ta na bibiyar kasar Sin. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China