in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta yi maraba da sanya hannu kan warware rikicin kan iyakokin kasashen Botswana da Namibia
2018-02-08 10:52:25 cri
Kungiyar tarayyar Afrika (AU) ta taya kasashen Botswana da Namibia murnar samun nasarar sanya hannu kan yarjejeniyar warware rikicin kan iyakokin kasashen biyu, wanda ya gudana a ranar Litinin a Windhoek, na kasar Namibia.

Sanya hannu kan yarjejeniyar ya kasance a matsayin cigaban da aka samu a kokarin da aka fara bisa ga bukatar da aka mikawa hukumar gudanarwar AU a shekarar 2015, kamar yadda AU din ta sanar a ranar Laraba.

Kungiyar ta Afrika mai mambobin kasashe 55, ta yabawa yarjejeniyar da cewa kyakkyawan yunkuri ne, kuma abin koyi ne ga dukkan mambobin kasashen kungiyar wajen warware dukkan takaddama da ta shafi kan iyakokin kasashen.

Sanarwar ta ce, sanya hannu kan yarjejeniyar ba kawai za ta kara karfafa dangantaka tsakanin kasashen Botswana da Namibia ba ne, har ma za ta kara aniyar kasashen biyu na kyautata yanayin mu'amala tsakanin alummominsu da kuma samar da cigaba ga kasashen masu makwabtaka da juna.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China