in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Botswana: kasar Sin ta samu ci gaba sosai a kokarin kau da talauci
2018-08-28 19:30:47 cri
Mokgweetsi Masisi, shugaban kasar Botswana, yana shirin halartar taron kolin dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka FOCAC da zai gudana a birnin Beijing na kasar Sin. Kafin ya tashi zuwa kasar Sin, ya yi hira da wakilan wasu kafofin watsa labarai na kasar Sin, inda ya nuna yabo sosai kan ci gaban da kasar Sin ta samu a fannin kau da talauci.

A cewar shugaban, kasar Sin ta dauki manyan tsare-tsaren rage talauci, wadanda suka taimaka wajen inganta rayuwar mutane da yawa. Bisa kokarin da gwamnatin kasar Sin ta yi, an yi nasarar fitar da dimbin jama'ar kasar Sin daga kangin talauci, wanda ya kasance wani babban ci gaban da ba a taba ganin irinsa ba a duniya.

Kafin ya zama shugaban kasa, mista Masisi ya taba kula da aikin rage talauci. A cewarsa, kasar Botswana ta koyi fasahar kasar Sin ne don tsara shirin rage talauci a gida. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China