in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kamalla zaben shugaban kasa a Kamaru cikin lumana
2018-10-08 10:16:05 cri

Hukumomi a Kamaru, sun bayyana gamsuwarsu da zaben shugaban kasa da aka kammala da misalin karfe 6 na yammacin jiya Lahadi a kasar.

Darakta Janar na hukumar zabe ta kasar Essosse Erik, ya bayyanawa taron manema labarai da aka yi a birnin Yaounde cewa, baya ga wasu rumfunan zabe da aka kada kuri'a bisa tsari na tsaro a yankunan arewa maso yammaci da kudu maso yammacin kasar saboda yanayin da ake ciki a wuraren, an kada kuri'a ba tare da wata matsala ba a kasar da ma kasashen waje, yana mai cewa kawo yanzu, babu kiddidigar da za ta nuna adadin mutanen da suka kada kuri'a a sauran sassan duniya.

Nan take bayan kammala kada kuri'ar, ofisoshin hukumar na yankuna suka fara kirgen kuri'un da kowanne dan takara ya samu.

Hukumar zaben ta ce kimanin mutane 6,600,000 ne suka yi rejista a zaben na jiya Lahadi. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China