in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar IOM ta samar da agajin jin kai ga bakin haure a Libya
2018-09-29 15:55:21 cri
Hukumar kula da masu kaura ta duniya (IOM), ta samar da kayakin jin kai ga bakin haure sama da 500 dake cibiyoyin da ake tsugunar da su a Libya, bisa taimakon asusun tallafi na Tarayya Turai wato European Union Trust Fund.

Sanarwar da hukumar IOM ta fitar, ta ce sama da bakin haure 500 ne suka karbi kayakin agaji da aka raba, sun hada da katifu da barguna da kayakin tsafta a cibiyar Shuhada Al Nasr, sai dai kuma hukumar ta ce bukatun bakin hauren ya zarce wadannan.

Har ila yau, hukumar ta yi alkawarin ci gaba da samar da kayakin bukata ga bakin hauren hauren dake akwai.

Cibiyoyin dake karbar bakin haure a Libya na cike makil da mutanen da aka tsare ko wadanda hukumomin kasar suka ceto daga tekun Bahr Rum. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China