in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
IOM ta samu rahoton nutsewar 'yan cin rani a kalla 90 sakamakon nutsewar kwale kwalen a Libiya
2018-02-02 20:50:58 cri
Hukuma mai kula da harkokin bakin haure ta MDD IOM, ta ce ta samu rahoton rasuwar wasu 'yan ci rani da yawan su ya kai a kalla 90, bayan da kwale kwalen da suke ciki ya nutse a kusa da gabar ruwan kasar Libiya da sanyin safiyar Juma'ar nan.

Wakiliyar IOM a kasar Libiya Olivia Headon, ta ce an samu gawawwakin wasu mutum 10 da ruwa ya turo bakin gabar tekun, ciki hadda na 'yan Libiya 2 da kuma wasu 'yan kasar Pakistan su 8.

Madam. Headon ta ce akwai kuma wasu mutum biyu da suka tsira bayan da suka yi iyo zuwa bakin gabar ruwan, yayin da wani kuma masunta suka ceto su da jiragen su na kamun kifi.

Hukumar IOM ta ce tana ci gaba da bincike, domin samun cikakkun bayanai game da aukuwar hadarin, tare da duba yiwuwar tallafawa wadanda suka tsira.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China