in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta bukaci a kara taimakawa yankin Dafur akokarin da yake na bude babin zaman lafiya
2018-09-29 15:50:58 cri
Manyan jami'an MDD sun yi kira ga al'ummomin duniya da su ci gaba da mara baya ga yankin Dafur domin tabbatar da wanzuwar nasarorin da aka samu.

Mataimakiyar Sakatare Janar na MDD Amina Mohammed ce ta yi kiran yayin wani muhimmin taron kan Dafur da aka yi a gefen babban taron zauren majalisar na bana

Amina Mohammed ta ce an zuba kudi dala billiyan 16 ga aikin wanzar da zaman lafiya cikin shekaru 10 da suka wuce, baya ga kudaden da aka kashe ga ayyukan jin kai domin rage radadin da jama'a ke fuskanta. Ta ce yayin da yankin ke farfadowa daga yaki, lokaci ya yi da za a karfafa nasarorin da aka samu, tana mai cewa lokaci ya yi da ya kamata a dauki matakin tabbatar da yankin Dafur ya samu ingantuwa ta fuskar tsaro da ci gaba.

Tun a shekarar 2003 yakin basasa ya barke a yankin, abun da ya yi sanadin mutuwar dubban mutane tare da raba wasu kusan miliyan 2 da matsugunansu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China