in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhu na MDD ya tsawaita aikin shirin wanzar da zaman lafiya a Dafur zuwa ranar 13 ga watan Yuli
2018-06-30 16:56:32 cri
Kwamitin sulhu na MDD, ya amince da wani kuduri na tsawaita aikin shirin wanzar da zaman lafiya a Dafur na Sudan, zuwa ranar 13 ga watan Yuli.

A wani yunkuri da daukacin mambobin kwamitin suka amince da shi, kwamitin ya sabunta aikin shirin UNAMID a Dafur, wanda na hadin gwiwa ne tsakanin Tarayyar Afrika da MDD.

Kudurin ya kuma bukaci shirin ya ci gaba da daukan mataki kan duk wani abu dake masa barazana ko wadanda yake karewa.

Kwamitin MDD ne ya kafa UNAMID mai hedkwata a El Fasher na arewacin Dafur a ranar 31 ga watan Yulin 2007, bayan amincewa da kuduri mai lamba 1769.

Ayyukansa ya kunshi kare fararen hula da taimakawa wajen kai agajin jin kai da shiga tsakanin gwamnati da 'yan adawa da kuma warware rikici tsakanin al'ummomi. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China