in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumomin kasa da kasa sun gana a Sudan don ingiza shirin tattaunawar sulhu kan Darfur
2017-10-31 10:27:36 cri
A ranar Litinin aka bude taron tattaunawa tsakanin kungiyoyin sulhu na cikin gida da na kasa da kasa game da batun rikicin yankin Darfur a Khartoum babbar birnin kasar Sudan.

Wakilan al'ummomin yankin na Darfur, da gwamnatin Sudan, da wakilan MDD, da na kungiyar AU, da kuma na dakarun wanzar ta zaman lafiya na kungiyar tarayyar Afrika dake Darfur (UNAMID) sun shiga taron tattaunawar.

Da yake jawabi a lokacin bude taron, mataimakin shugaban kasar Sudan Hassabo Mohamed Abdul-Rahman, ya bayyana cewa, yankin Darfur yana samun kyautatuwa sakamakon yarjejeniyar da aka kulla ta birnin Doha game da zaman lafiyar yankin wato (DDPD) a takaice.

Ya nanata muhimmancin cigaba da tattaunawar da dukkan bangarorin da abin ya shafa domin kawo karshen tashin hankali a yankin.

Haka zalika, wakilin musamman na UNAMID, Jeremiah Mamabolo, ya bukaci kungoyoyin 'yan tawaye da ba su sanya hannu kan yarjejeniyar ba da su amince su shiga tattaunawar.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China