in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin wajen Sin ya soki zargin da aka yiwa kasarsa game da tsoma hannu cikin harkokin wata kasa
2018-09-27 09:00:04 cri
Babban dan majalissar zartaswa, kana ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya soki zargin da aka yiwa kasarsa, game da yunkurin tsoma hannu a harkokin zaben tsakiyar zangon shugabancin gwamnatin Amurka mai ci, yana mai cewa zargin ba shi da tushe bare makama.

Wang Yi ya ce ko da a baya, kasar Sin ba ta taba tsoma baki a harkokin cikin gidan wata kasa ba, ba kuma za ta yi hakan a yanzu ko a nan gaba ba.

Ministan ya ce kauracewa shiga sharo ba shanu, al'ada ce ta gargajiya da aka san Sin a kai, take kuma samun yabo bisa riko da ita, ba kuma za ta sauya daga wannan matsaya ba.

Daga nan sai ya yi kira ga kasashen duniya, da su yi riko da wannan ka'ida ta MDD, wadda ta haramta daukar duk wani mataki, na tsoma baki a harkokin sauran kasashe na daban. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China